THE CANTICLES IN HAUSA

1 Tarihi 29:10-13

Yabo gare ka, Yahweh, * Allah na kakanmu Yakubu, * tun fil'azal har abada.

    Girma da iko naka ne, Yahweh, * da daraja da nasara da ]aukaka.

    Dukan abin da ke a sama da }asa naka ne, Yahweh, * da mulki da sarautar kome da kome.

    Wadata da ]aukaka daga wajenka suke, * kai ne ke mulkin duk kome.

    Daga hannunka ke }ar}o da iko, * daga hannunka ke girma da sarautar duk kome.

Yanzu, ya Allahnmu, muna gode maka, * muna yabon sunanka mai daraja.

1 Sama'ila 2:1-10

Zuciyata tana murna da Yahweh, * ina samun }arfi daga wurin Yahweh.

Ina yi wa ma}iyana dariya, * ina matu}ar murna domin ka taimake ni.

    Babu wani mai tsarki kamar Yahweh, * babu Dutse kamar Allahnmu.

    Kada ku }ara yin magana ta girman kai, * kada fahariya ta fito daga bakinka.

    Gama Yahweh Allah ne masani, * Mai Iko ne wanda ke auna ayyuka.

        An kakkarya bakan jarumai, * amma aka sa wa raunannu }arko.

        {osassu suna wadago don abinci, * amma mayunwata ba su bukatar aiki.

            Bakarariya ta haifi 'ya'ya bakwai, * amma mai yawan 'ya'ya ta rasa su.

            Yahweh na kashewa, ya kuma rayar, * yana kai wa Shawol, ya ma jawo.

            Yawheh na talautarwa, ya ma arzuta, * yana }as}antarwa, ya ma ]aukaka.

        Yana ]aga matalauta daga }ura, * ya tā da mabukata daga wurin bola,

        don ya zaunad da su tare da 'yan sarakuna, * ya ba su kursiyi mai daraja.

    Domin harsassan duniya na Yahweh ne, * a kansu ya kafa duniya.

    Yana lura da tafiyar masu bautarsa, * amma miyagu za su halaka a Duhu.

    Domin ba }arfin mutum ke sa ya yi nasara ba, * Yahweh zai kakkarya masu yi masa tawaye.

Ma]aukaki zai tsautar daga sama, * Yahweh zai hukunta har iyakokin duniya.

Zai ba sarkinsa iko, * ya tā da }arfin shafaffen sarkinsa.

Daniyel 3:26-7,29,34-41

Yabo gare ka, Yahweh, Allah na kakanninmu, * sunanka ya cancanci yabo da ]aukaka har abada.

    Gama kai mai adalci ne a duk abin da ka yi mana, * dukan ayyukanka na gaskiya ne.

    Hanyoyinka kuma ba su da aibu, * ai, dukan shari'unka na zahiri ne...

        Ai, ta zunubanmu da }in manufa ne, * muka bau]e maka.

        Mun yi sa~o a kowane abu, * ba mu yi biyayya da dokokinka ba....

            Don darajar sunan nan naka, * kada ka ba da mu kwatakwata, * kada ma ka zare yarjejeniyarka.

            Kada ma ka janye jin}anka daga gunmu, * saboda Ibrahim }aunataccenka,

            da kuma Isiyaku bawanka, * da mai tsarkin nan naka, Isra'ila,

                wa]anda ka yi alkawari ta kansu, cewa * jikokinsu za su yi yawan gaske,

                kamar taurarin sama, * ko rairayin da ke bakin teku.

            Yanzu, Yahweh, mun fi sauran al'ummai salwanta, * an ma yi mana }as}anci kwanan nan a dukan duniya, * saboda zunubanmu ne kuwa.

            A wannan lokaci ma ba mu da sarki ko annabi, ko shugaba, * ba hadayar }onawa, ko hadaya, ko baiko, ko turaren }onawa,

            ba gun da za a mi}a hadaya a gabanka, * ta neman jin}ai.

        Duk da haka, don muna da karyayyar zuciya da ruhun tuba, * sai ka kar~e mu.

        Kamar dai yadda ka kar~i hadayun }onawa na raguna da na bajimai, * da kuma na 'ya'yan raguna masu ki~a dubbai bisa dubbai,

        haka ma ka kar~i hadayarmu ta yau, * domin muna binka sau da }afa.

    Gama duk wanda ya dogara gare ka, * ko ka]an ba zai kunyata ba.

Yanzu mun bi ka da dukan zuciya, * kanmu }asa, hannunmu baya, * muna neman fuskarka.

Daniyel 3:57-88,56

Maimaitawa: Ku yabe shi, ku girmama shi har abada.

Ku yabi Yahweh, ayyukan Yahweh duka, * ku yabi Yahweh, mala'ikun Yahweh.

Ku yabi Yahweh, sammai da birbishin }asa, * ku yabi Yahweh, ruwayen birbishin duniya.

Ku yabi Yahweh, dukan ikokinsa, * ku yabi Yahweh, rana da wata masu haske.

Ku yabi Yahweh, taurarin sama, * ku yabi Yahweh, tsattsafi da ra~a.

Ku yabi Yahweh, iska da hadari, * ku yabi Yahweh, wuta da zafi.

Ku yabi Yahweh, jaura da sanyi, * ku yabi Yahweh, }an}ara da dusar }an}ara.

Ku yabi Yahweh, dare da rana, * ku yabi Yahweh, haske da duhu.

Ku yabi Yahweh, wal}iya da girgije, * ki yabi Yahweh, ya ke duniya.

Ku yabi Yahweh, duwatsu da tuddai, * ku yabi Yahweh, mabun}usa }asa.

Ku yabi Yahweh, ma~u~~ugan ruwa, * ku yabi Yahweh, tekuna da koguna.

Ku yabi Yahweh, kifaye manya da }anana, * ku yabi Yahweh, tsuntsayen sama.

Ku yabi Yahweh, dabbobin duniya, * ku yabi Yahweh, 'yan adan.

Ku yabi Yahweh, Isra'ilawa, * ku yabi Yahweh, firistocin Yahweh.

Ku yabi Yahweh, bayin Yahweh, * ku yabi Yahweh, masu halin adalci.

Ku yabi Yahweh, tsarkaka masu sanyin hali, * ku yabi Yahweh, Hananiya, da Azariya, da Mishayel.

Yabo ya tabbata gare ka a sararin sama, * a yabe ka, a girmama ka har abada.

Daniyel 3:52-57

Yabo gare ka, Yahweh, Allah na kakanninmu, * a yabe ka, a girmama ka har abada.

Yabo ga tsattsarkan sunanka mai daraja, * a yabe ka, a girmama ka har abada.

Yabo gare ka a Haikalin ]aukakarka mai tsarki, * a yabe ka, a girmama ka har abada.

Yabo gare ka, a bisa kursiyinka, * a yabe ka, a girmama ka har abada.

Yabo gare ka, wanda ke zaune a bisa kerubobi, * a yabe ka, a girmama ka har abada.

Yabo gare ka, mai duba zurfin duniya, * a yabe ka, a girmama ka har abada.

Yabo gare ka a sararin sama, * a yabe ka, a girmama ka har abada.

Ku yabi Yahweh, ayyukan Yahweh, * ku yabe shi, ku girmama shi har abada.

Maimaitawar Shari'a 32:1-12

Ku saurara, ku sammai, zan yi magana, * bari duniya ta ji kalmar bakina.

Bari koyarwata ta zubo kamar ruwan sama, * kalmata ta fa]o kamar ra~a,

kamar yayyafi a bisa ]anyar ciyawa, kamar ]i]]igar ruwa a bisa ganyaye.

    Gama zan yi shelar sunan Yahweh. * Ku yabi girman Allahnmu!

    Dutsen nan, aikinsa cikakke ne, * dukan hanyoyinsa masu adalci ne.

    Allah mai aminci ne, baya yaudara, * mai adalci ne, mai kirki.

        Sun aikata }eta a gabansa, * su ba 'ya'yansa ba ne saboda lalacewarsu, * su muguwar tsara ce, karkatacciya.

        Haka za ku sāka wa Yahweh, * ku wawaye marasa hikima.

        Ba shi ne Ubanku, Mahaliccinku ba, * wanda ya yi ku, ya kuma kafa ku?

            Ku fa tuna da kwanakin dā, * ku yi tunani a kan shekarun da suka wuce.

            Ku tambayi mahaifanku, za su fa]a maku, * ku tambayi dattawanku, su za su gaya maku.

        Sa'ad da Ma]aukaki ya ba al'ummai gādonsu, * sa'ad da ya raba 'yan adan,

        ya auna iyakokin al'ummai, * don kowacensu ta sami ]an allahnta.

        Amma Yahweh ya za~i Isra'ila don kansa, * Yakubu shi ne rabon gādonsa.

    Ya same shi a cikin hamada, * a jeji mai rurin iskoki.

    Ya kewaye shi, ya lura da shi, * ya kiyaye shi kamar }wayar ido.

Kamar gaggafar da ke lura da she}arta, * tana rufe 'ya'yanta,

haka ya mi}a fukafukansa, ya ]auke shi, * ya tafi da shi a kan fukafukansa.

Yahweh ne ka]ai ya bishe shi, * ba wani ba}on allah tare da shi.

Fitowa 15:1-4a,8-13,17-18

Zan raira wa}a ga Yahweh, * gama ya ci gawurtacciyar nasara.

Doki da mahayinsa * ya jefar cikin bahar.

Yahweh }arfina ne, ina yabonsa, * shi ne wanda ya cece ni.

    Wannan ne Allahna, zan girmama shi, * Allah na kakana, zan ]aukaka shi.

    Yahweh maya}i ne, * sunansa Yahweh.

        Karusan Fira'auna da rundunarsa * ya jefar cikin bahar...

        Da hucin lumfashin hancinka * ruwa ya tattaru.

        Rigyawa ta tsaya kamar tudu, * zurfafan ruwaye suka daskare a tsakiyar bahar.

            Magabcin ya ce, * "Zan bi, in kama su,

            in kwashi ganima, * muradina a kansu zai biya,

            zan zare takobina, * hannuna zai halaka su."

                Ka hura iskarka, * bahar ta rufe su,

                suka nutse kamar darma * cikin manyan ruwaye.

            Yahweh, wanene kamarka cikin alloli? * wa ke kamarka cikin ]aukaka da tsarki?

            Mai banrazana ta yin al'ajibai, * mai aikata mu'ujjiza.

            Ka mi}a hannunka na dama, * }asa ta ha]iye su.

        Amma da }aunarka ka ja gorar * jama'arka da ka fansa.

        Ka bi da su da }arfinka * zuwa tsattsarkan mazauninka...

    Za ka kawo su, ka dasa su * a kan dutsen da ka za~a,

    wurin mazauninka, * wanda kai, Yahweh, ka kafa,

    tsattsarkan wurinka, ya Ubangiji, * wanda hannuwanka suka yi.

Yahweh zai yi mulki * har abada abadin.

Ezekiyel 36:24-28

Ga abin da Ubangiji Yahweh ya fa]i: * "Zan kwaso ku daga cikin al'ummai,

in tattaro ku daga dukan }asashe, * in kawo ku cikin }asarku.

    Zan yayyafa maku tsabtaccen ruwa, * za ku kuwa tsarkaka daga dukan }azantarku. * Zan tsarkake ku daga dukan gumakanku.

        Zan ba ku sabuwar zuciya, * in sa sabon ruhu a cikinku.

        Zan cire zuciyar dutse daga gare ku, * sa'an nan in sa maku zuciyar nama.

    Zan sa ruhuna a cikinku, * in sa ku bi ka'idodina, * ku himmanta ga aikata hukuntaina.

Za ku zauna cikin }asar * da na ba kakanninku.

Za ku zama mutanena, * ni kuma in zama Allahnku."

Habakuk 3:2-4,13a,15-19

Yahweh, na ji labarinka, * Yahweh, ayyukanka sun ba ni tsoro.

Ka maimaita su a zamaninmu, * a kwanakinmu ka sanar da su! * Duk da fushinka, ka tuna da yin jin}ai.

    Daga Teman Allah ke fitowa, * daga Dutsen Faran Tsattsarkan nan ke tahowa.

    [aukakarsa ta rufe sammai, * duniya kuwa ta cika da girmansa.

        {yallinsa yana annuri kamar hasken rana, * wal}iyoyi na fitowa daga hannuwansa, * can ne ma~oyin ikonsa...

    Ka fito saboda ceton jama'arka, * saboda ceton shaffafen sarkinka...

    Da dawakanka ka tattake teku * da haukan ruwa mai }arfi.

    Da na ji, sai jikina ya yi rawa, * le~unana suka raurawa,

    }asusuwana suka rabke, * }afafuna suka girgiza.

        Amma da kwanciyar rai ina jiran masifar * da za ta auko wa wa]anda suka kawo mana ya}i.

    Ko da yake itacen ~aure bai yi toho ba, * ba kuma 'ya'ya a kuringar inabi,

    zaitun kuma bai ba da amfani ba, * gonaki ba su ba da abinci ba,

    tumaki sun ~ace daga garke, * ba kuma shanu a turaku,

    duk da haka zan yi farinciki da Yahweh, * in yi murna da Allah Macecina.

Yahweh Ubangijina shi ne }arfina, * yana sa in yi tsalle kamar barewa, * yana kuma bishe ni zuwa kan duwatsu.

Ishaya 2:2-5

A kwanaki masu zuwa, * dutsen gidan Yahweh zai kafu

bisa sauran duwatsu, * zai fi dukan tuddai tsawo.

Dukan al'ummai za su malalo gare shi, * mutane masu yawa za su zo, su ce:

    "Bari mu je dutsen Yahweh, * zuwa gidan Allah na Yakubu,

    don ya koya mana hanyoyinsa, * mu kuwa bi labobinsa.

    Domin dokokinsa na fitowa daga Sihiyona, * maganar Yahweh kuwa daga Urushalima.

    Zai hukunta tsakanin al'ummai, * zai shari'anta mutane masu yawa.

Za su na]e takubbansu su zama garemani, * masunsu ma su zama laujuna.

Al'umma ba za ta yi ya}i da wata al'umma ba, * ba za su }ara koyon ya}i ba.

Gidan Yakubu, zo, * mu yi tafiya da hasken Yahweh.

Ishaya 12:1-6

Ina yabonka, Yahweh, ko da yake ka yi fushi da ni, * gama fushinka ya wuce, ka yi mani ta'aziya.

    Hakika, Allah ne Macecina, * ina da sazuciya, bana tsoro.

        Yahweh }arfina ne, ina yabonsa, * Yahweh ne wanda ya cece ni.

    A ranan nan za ku jawo ruwa da farinciki * daga idon ruwan ceto,

    kuna cewa: "Ku gode wa Yahweh, * ku yi kirarin sunansa.

        Ku sanar wa al'ummai al'ajibansa, * ku bayyana yadda sunansa yake da girma.

    Ku raira wa}a ga Yahweh saboda manyan ayyukan da ya yi, * bari dukan duniya ta ji labarin.

Mazaunan Sihiyona, ku yi sowa da wa}a, * domin Tsattsarkan nan na Isra'ila girma gare shi a cikinku.

Ishaya 26:1-4,7-9,12

Muna da birni }a}}arfa, * garunsa da ganuwarsa na tsare mu.

Ku bu]e }ofofinsa, * a bar al'umma mai gaskiya ta shiga.

Suna kiyaye aminci, * aniyarsu ta tabbata.

    Kana ba su cikakkiyar salama, * domin sun dogara gare ka.

    Ku dogara ga Yahweh har abada, * domin Yahweh madauwamin Dutse ne...

        Hanyar mai gaskiya daidai take, * kana mai da labinsa bai ]aya sumul.

        I, ta bin hanyar hukuntanka, * Yahweh, muna sa zuciya gare ka.

    Sunanka da shahararka, * su ne abin da muke marmari.

    Raina yana marmarinka da dare, * ruhuna a cikina yana begenka.

Gama da hukuntanka suka zo duniya, * mazaunanta sun koyi gaskiya...

Yahweh, kā }addara mana salama, * domin dukan ayyukanmu, kai ne ka yi su.

Ishaya 33:13-16

Ku da ke nesa, ku ji abin da na yi, * ku da ke kusa, ku gane ikona!

A Sihiyona masu zunubi ke firgita, * makyarkyata ta kama marasa ibada, suka ce:

"Wanene daga cikinmu zai iya zama da wutan nan mai cinyewa? * Wanene daga cikinmu zai iya zama da dauwamiyyar gobara?"

    Wanda ya bi adalci, ya yi maganar gaskiya, * ya }i ku]in cuta,

    ya hana hannuwansa kar~ar toshi, * ya toshe kunnuwansa ga maganar kisan kai, * ya rufe idanunsa ga muguwar dabara,

wannan zai zauna a wurin mai sama, * mafakar duwatsu matserarsa ce.

Za a kai masa abincinsa, * ruwan shansa ba zai }are ba.

Ishaya 38:10-14,17b-20

Na ce, "A ga~ar }arfina * ina ta }aura.

An sanya ni a }ofofin Shawol * sauran rayuwata."

Na ce, "Ba zan }ara ganin Yahweh * a duniyar masu rai ba.

Ba zan }ara ganin mutun * gun mazaunan Gidan Hutu ba."

    An tum~uke ]akina, an na]e shi * an ]aukan mani shi kamar alfarwar makiyayi.

    Kamar masa}i kā na]e rayuwata, * kā yanke ta daga gindin saa.

        Da rana da dare kana tsananta mani, * ina ta kuka dukan dare.

        Kamar zakin da ke kakkarya }asusuwana, * kana tsananta mani dukan yini.

        Ina kuka da ~acin rai kamar tsattsewa, * kamar kurciya ina ta yin wa}ar makoki.

        Idanuna na duban sama da gajiya, * ya Ubangiji, ina shan wahala, ka lura da ni...

    Kā hana raina * shiga Ramin Halaka.

    Kā jefa dukan zunubaina * a bayanka.

Gama Shawol ba za ta gode maka ba, * Mutuwa ma ba za ta yabe ka.

Masu gangara wa Kabari * ba su jiran tausayinka.

    Sai dai masu rai ne za su yabe ka, * kamar yadda nike yi yau.

    Uba zai fa]i * wa 'ya'yansa amincinka.

Yahweh, ka cece mu, * za mu kuwa yi maka wa}a

dukan kwanakin rayuwarmu * a gidan Yahweh.

Ishaya 40:10-17

Ga shi, Ubangiji Yahweh na zuwa da iko, * yana mulki da }arfin dantsensa.

Ya rigaya ya sami lada, * yana da amfanin aikinsa.

Kamar makyayi ne yana kiwon garkensa, * yana tattara 'yan raguna da hannuwansa,

yana rungumarsu a }irjinsa, * yana bi da tumaki kuma.

    Wa ya ta~a }irga yawan ruwan teku da hannunsa, * ko ya auna sararin sama da tafinsa?

    Wa ya ta~a }irga yawan }asa da buhu, * ko ya auna nauyin duwatsu a ma'auni da tuddai da mizani?

        Wa ya ta~a auna ruhun Yahweh, * ko ya zama mashawarcinsa mai ba shi labari?

    Wa ya ta~a shawarta don ya fahimce shi, * ya kuwa koya masa hanyar hukunci,

    ya koya masa ilimi, * ya nuna masa hanyar fahimi?

A gare shi, al'ummai kamar ]igon ruwa ne a bokiti, * ko }ura bisa ma'auni, * garuruwan da ke ga~ar teku ba su fi toka nauyi ba.

Kurmin Labanan baya da isasshen icen wuta, * ko dabbobin da ake bukata don baikon }onawa.

Dukan al'ummai ba kome ba ne a gare shi, * banza a banza ne gunshi.

Ishaya 42:10-16

Ku raira sabuwar wa}a ga Yahweh, * har bangon duniya ku yabe shi,

ku masu tafiya a kan teku da duk da ke cikinsa, * }asashen da ke ga~ar teku da mazaunansu.

    Ku ta da murya, ku }auyukan daji, * da sansanan mutanen Kedar kuma!

    Ku yi sowa, ku mazaunan garin Dutse, * ku yi kururuwa daga }wan}olin duwatsu!

    Ku yi shelar ]aukakar Yahweh, * ku yabe shi da mutanen da ke gefen teku!

        Yahweh na fita kamar jarumi, * kamar maya}i yana ta da aniyarsa.

        Yana gunzar kirarin ya}i, * yana kai wa magabtansa hari, yana cewa:

        "Na da]e ina yin shiru, * ina ha}uri ba tare da magana ba.

        Amma yanzu ina kamar macen da ke na}udda, * ina }ugi da nishi da haki.

    Zan lalatar da duwatsu da tuddai, * in busar da dukan ciyawarsu.

    Zan mai da kwaruruka hamada, * in busar da fadamu.

Sa'annan zan yi wa mutanena makafi jagora * a hanyoyin da ba su ta~a bi ba.

A kan labunan da ba su sani ba * zan bi da su.

Zan sa duhu ya zama haske a gabansu, * karkatacciyar hanya ta zama daidai.

Ishaya 45:15-25

Lalle, kai ne ~oyayyen Allah, * ya Allah na Isra'ila Maceci.

    Masu yin gumaka * sun kunyata, sun sha }as}anci,

        dukansu tare, * sun zama abin kunya.

        Amma ceton Isra'ila daga wurin Yahweh yake, * dauwamammen ceto ne.

    Ba za su kunyata ko su sha }as}anci ba * a zamanai duka nan gaba.

    I, Yahweh ne, * Mahallicin sama,

        Allah ne, * wanda ya shata }asa, ya yi ta, ya kafa ta.

            Bai halicce ta hamada ba, * amma wurin zaman mutane.

            In ji shi, "Ni ne Yahweh, * ba wani Allah.

        Ba a ~oye na yi magana ba, * ko a duhun lungun duniya.

    Ban ta~a cewa da jikokin Yakubu, * 'Ku neme ni a hamada' ba.

Amma ni, Yahweh, ina fa]in gaskiya, * ina sanar da abin da ke daidai.

Ku tattaru, ku zo wuri guda, * ku masu tsira ta gudun hijira.

    Ba su san kome ba, * su da ke ]aukar gumakansu na ice,

        suna addu'a ga allolin * da ba su iya yin ceto.

        Bari su yi magana, su gabatar da matsalarsu, * su shawarci juna.

    Wanene ya sanar da abin da zai faru tun dā, * ya kuma yi annabci tuntuni?

        Ashe, ba ni ba ne, * Yahweh Allah, * da ba wani sai ni?

            Ba Allah na gaskiya, * mai yin ceto, sai ni.

            Ku juyo gare ni don ku ku~uta, * ya mutanen ko'ina a duniya,

        domin ni ne Allah, * ba wani.

    Na yi rantsuwa da kaina, * na fa]i gaskiya, * ba canjin abin da na }addara:

        Gwiwar kowa za ta dur}usa a gabana, * kowa zai yi shahada, cewa:

        'Daga Yahweh ne * nasara da iko ke zuwa.'"

    Amma duk masu yi masa tawaye * za su zo gabansa da kunya.

Ta wurin Yahweh dukan jikokin Isra'ila * za su sami nasara da ]aukaka.

Ishaya 61:10- 62:5

Ina farinciki }warai da Yahweh, * na yi murna da Allahna.

Domin ya suturce ni da rigar ceto, * ya sa mayafin nasara a kaina.

Ina kamar angon da ya sa rawani, * kamar amaryar da ta sa adonta.

    Kamar yadda }asa ke fitad da tohonta, * lambu kuma ke tsirad da yabanya,

    haka Yahweh zai sa gaskiya da yabo * su tsira a gaban dukan al'ummai.

        Ba zan yi shiru a kan Sihiyona ba, * ba kuwa zan bebance game da Urushalima ba,

        sai cetonta ya fito kamar haske, * nasararta kuma ta haskaka kamar fitila.

            Al'ummai za su ga nasararki, * dukan sarakunansu kuma ]aukakarki.

        Za a kira ki da sabon suna, * wanda bakin Yahweh zai ra]a.

        Za ki zama kambin ]aukaka a hannunYahweh, * da rawanin mulki a hannun Allahnki.

    Ba za a }ara kiranki "Korarriya" ba, * ko }asarki "Kufai",

    Amma za a kira ki "aunatacciya", * da }asarki "Amarya".

    Gama Yahweh na jin da]inki, * don yana auren }asarki.

Kamar yadda saurayi ke auren matarsa, * haka Mai Gininki zai aure ki.

Kamar yadda ango ke murna da amaryarsa, * haka Allahnki zai yi murna da ke.

Ishaya 66:10-14

Ku yi murna tare da Urushalima, * duk masu sonta, ku yi farinciki tare da ita!

Ku yi murna tare da ita yanzu, * dukanku da kuka yi makoki dominta!

    Yanzu ku sha, ku }oshi * daga mamanta na ta'aziya.

    Yanzu ku sha, ku ji da]i * daga }irjinta mai yawan nono.

        Gama, in ji Yahweh, * "Yanzu ina sa salama ta malalo mata kamar kogi, * da wadatar al'ummai kamar rigyawa.

    Za ta goye ku, ta yi renonku, * za ta kuma rungume ku a }irjinta.

    Kamar yadda uwa ke ta'aziyar yaronta, * haka ni zan yi ta'aziyarku, * za ku ta'azantu a Urushalima.

Da kuka ga wannan zuciyarku za ta faranta, * jikunanku kuma za su yi yabanya kamar ciyawa.

Irmiya 14:17-21

Idanuna suna zub da hawaye * dare da rana,ba denawa,

saboda babbar masifar da ta faru * ga budurwar da ke jama'ata, * sai ta raunana }warai.

    Idan na tafi cikin saura, * sai in ga wa]anda aka kashe da takobi.

    Idan na shiga birni, * sai in ga wa]anda ke fama da yunwa.

    Har annabi da firist * suna yawon neman abinci inda ba su san kowa ba.

        Ka }i Yahuda ke nan ]ungum? * ranka kuma yana jin }yamar Sihiyona ne?

    Me ya sa ka buge mu, * har da ba za mu iya warkewa ba?

    Muna zuba ido ga samun salama, * amma ba wani alheri da ya zo.

    Muna sa zuciya ga warkewa, * amma sai razana.

Yahweh, mun san muguntar da muka yi, * da wadda kakanninmu suka yi, * gama mun yi maka zunubi.

Saboda darajar sunanka, kada ka yashe mu, * kada kuma ka rena Sihiyona, kursiyin ]aukakarka.

Ka tuna da yarjejeniyar da ka yi mana, * kada ka ta da ita.

Irmiya 31:10-14

Ku ji maganar Yahweh, ku al'ummai, * ku yi shelarta har }asashen hayin ruwa.

Ku ce: "Wanda ya warwatsa Isra'ila zai tattaro shi, * zai kiyaye shi kamar yadda makiyayi yakan kiyaye garkensa."

Gama Yahweh ya fanshi Yakubu, * ya ciro shi daga hannun da ya fi shi }arfi.

    Za su zo su yi wa}a a bisa }wan}olin Sihiyona, * za su gudano ga alheran Yahweh,

    ga hatsi da abinshan inabi da mai, * ga 'yan raguna da na shanu.

    Rayuwarsu za ta zama kamar lambu, * ba za su }ara yin yaushi ba.

    'Yan mata za su yi rawa da farinciki, * samari da tsofaffi za su yi murna.

Zan mai da makokinsu ya zama murna, * in ta'azantar da su, in ba su farinciki maimakon ba}inciki.

Zan wadaci firistoci da abinci mai yawa, * jama'ata kuma za su }oshi da alherina.

Bayahudiya 16:1-2,13-16

Ku soma yi wa Allahna wa}a da tambura, * ku yi wa Yahweh yabo da kuge.

Ku raira masa sabuwar wa}a mana, * ku ]aukaka shi, ku kuma kira bisa sunansa.

    Gama Allah mai tattake ya}e-ya}e, * shi ne Yahweh...

    Ai, dole in raira wa Allahna sabuwar wa}a., * Yahweh, ai, kai mai girma ne da ]aukaka, * mai tsananin iko, ba mai iya karawa da kai.

        Ka sa dukan halittunka su yi maka hidima, * gama magana kawai ka yi, sai suka wanzu.

        Kai ne ka aiko da numfashinka, ka halitta su, * ai, ba mai iya yin jayayya da kalmarka.

    Gama ko da an jijjige gindin tsaunuka da zurfin tekuna, ko da duk duwatsu sun narke kamar dano a gabanka,

    ga masu tsoronka * za ka nuna jin}ai.

Gama kowace irin hadaya mai }anshi }aramar aba ce, * haka ma hadayun }onawa masu kitse.

Amma duk mai tsoron Yahweh, * shi ne mai girma har abada.

Hikima 9:1-6, 9-11

Ya Allah na kakannina, Ubangijin jinai, * wanda ka halicci kome ta kalmarka,

ta hikimarka ka sifanta mutun, * don ya mallaki abubuwan da ka halitta,

ya mallaki duniya da tsarki da adalci, * ya zartad da shari'a da adalcin zuciya,

    ka ba ni hikimar da ke kewaye da kursiyinka, * kada ma ka ware ni daga cikin 'ya'yanka,

        gama ni bawanka ne * kamar yadda iyayena suke dā,

        mutun ne kuma, ina da kwanakin rai 'yan ka]an, * na kasa gane shari'a da ka'idodinka.

            Ko da ]an adan ya zama cikakke, * in ya rasa hikimarka zai fā]i ba nauyi...

        A wurinka hikima take wadda ta san aikinka, * a kan idanunta ne ma lokacin da ka halicci duniya,

        ta san abin da ke faranta maka rai, * da kuma abin da ya wajaba a bi cikin dokokinka.

    Sai ka kwararo ta daga sammanka masu tsarki, * ka ma aiko ta daga kursiyin ]aukakarka,

don ta zauna da ni, ta yi aiki a cikina, * ai, ta haka ne zan san abin da ke daidai a gabanka.

Gama ita ta sani, ta kuma gane dukan kome, * za ta kāre ni da himma a cikin aikina, * ta bi da ni da ]aukakarta.

Sirak 36:1-5,10-13

Ka cece mu, ya Allah na dukan halitta, * ka sa sauran al'ummai su ji tsoronka.

Ka nuna wa ma}wabtan al'ummai }arfi, * domin su ga ikonka zahiri.

    Yadda ka hore mu domin ka nuna masu tsarkinka, * ka hore su, su ma, domin ka nuna mana ]aukakarka.

    Ka sa su san ka, yadda muka san ka, * su sani, ba wani Allah sai dai kai.

        Ka koma wa aikinka na al'ajabi, ka yi sababbin alamu, * tashi, ka gwada dantsenka....

        Ka tara dukan kabilan Yakubu, * don su gaji }asarsu, kamar yadda yake a dā.

    Ka yi jin}ai a kan al'ummar da ake kira da sunanka, * a kan Isra'ila wanda ka kira ]an farinka.

    Ka ji }an tsattsarkan birninka, * Urushalima, mazaunin zatinka.

Ka cika Sihiyona da darajarka mai girma, * Haikalinka kuma da ]aukakarka.

Tobi 13:2-8

Yabo ga Allah wanda ke raye har abada, * gama mulkinsa ya tabbata har abada!

Yana raunanawa, yana yin jin}ai, * yana aikawa da mutane Zurfafan Lahira,

ya kuma zaro su daga babbar halaka, * ai, ba mai iya ku~uta daga hannunsa.

    Ku yabe shi a gaban al'ummai mana, ku Isra'ilawa, * ai, ko da ya yi ]ai]ai da ku a tsakaninsu, * a can ma ya nuna muku ikonsa a fili.

    Ku ]aukaka shi a gaban dukan mutane, * gama shi ne Yahweh Allahnmu, * shi ubanmu ne da Allahnmu, har abada abadin.

        Ko da yake ya hore ku a kan zunubanku, * ai, zai ma ji tausayin dukanku.

        Zai tattaro ku gu ]aya daga sauran al'ummai, * daga duk inda aka yi ]ai]ai da ku a dā.

            In dai kun juya gare shi da dukan zuciyarku, * kuna aikata aikin gaskiya a gabansa,

            Sa'annan zai juyo gare ku, shi ma, * ba kuma zai }ara ~oye muku fuska ba.

            Ku dubi dai irin abin kirkin da ya yi muku, * ku gode masa mana, kai jama'a!

            Ku yabi Ubangijin adalci, * ku kuma ]aukaka Sarkin dukan zamanai!

        Ai, ni ma nakan yi wa}ar yabonsa * a lokacin da nake bawan ya}i a wani gari.

        Na sanar da ikonsa da girmansa a fili * ga al'ummar da take yin sa~o.

    Ai, ku masu sa~o, sai ku juya gunsa, * ku dai kasance da hali mai kyau.

    Lalle zai yi muku alheri, * ya kuma ji tausayinku.

Ni ma ina ]aukaka Allah, * raina kuma yana yin fari fat da Sarkin nan na Sama.

Bari girmansa ya zauna a bakin dukan mutane, * a yi wa}ar yabonsa a Urushalima.

Tobi 13:8-14

Bari girmansa ya zauna a bakin dukan mutane, * a yi wa}ar yabonsa a Urushalima.

Ya Urushalima, birni mai tsarki, * Allah ya raunana ki a kan gumakan da kika yi, * amma duk da haka zai ji tausayin 'ya'yanki, adalai.

    Ki gode wa Allah saboda alherinsa, * ki yabi Sarkin dukan zamanai!

    Domin za ki yi farinciki * da ganin an sāke gina masujadarsa a cikinki.

    Zai kuma dawo miki da bayin ya}inki, * ya ta'azanta su a cikinki.

    Dukan wa]anda ke ba}inciki zai }aunace su a cikinki, * har dukan zamanai masu zuwa.

        Ai, hasken haske zai haskaka * a kan duk sashe na duniya.

            Kabilai za su bangazo gare ki daga wurare masu nisa, * daga wannan bangon duniya zuwa wancan, * domin su ji labarin alherin da Yahweh ya yi miki,

        suna da kyautai a hannunsu * domin Sarkin Sama.

    A cikinki, tsara za ta bi tsara, * suna bayyana matu}ar farincikinsu a kanki.

    Har ga 'yan zamanin nan na gaba, * kowa zai san Allah ya za~e ki.

    Yanzu dai, sai ki yi murna * da 'ya'yanki adalai,

    gama za a tara su duka a gu ]aya, * su yabi Ubangijin dukan zamanai.

Albarka ta tabbata gun masu }aunarki, * da wa]anda ke na'am da zaman alamarki.

Masu albarka ne kuma su da suka yi makoki * a kan dukan wahalarki.

Filibiyawa 2:6-11

Ko da yake surar Allah yake, * Yesu bai mai da daidaitakan nan tasa da Allah * abar karabkiya ba,

sai ma ya mai da kansa baya matu}a * ta ]aukar surar bawa, * da kuma kasancewa da kamannin ]an'adan.

    Da ya bayyana da siffar mutum, * sai ya }as}antad da kansa ta yin biyayya,

        har wadda ta kai shi ga mutuwa, * mutuwar ma ta kan gicciye.

    Saboda haka ne kuma Allah ya ]aukaka shi mafificiyar ]aukaka, * kuma ya yi masa baiwa da sunan nan * da ke birbishin kowane suna,

don dai kowace gwiwa sai ta rusuna * wa sunan nan na Yesu, * a sama da }asa, da kuma can }ar}ashin }asa,

kowane harshe kuma ya yarda cewa * Yesu Almasihu Ubangiji ne, * don ]aukaka Allah Uba.

Wahayin Yahaya 19:1,5-8

Halelu-Yah! Yin ceto, da ]aukaka, da iko, sun tabbata ga Allahnmu,       Halelu-Yah!

    don hukuncinsa daidai yake, kuma na gaskiya ne.                        Halelu-Yah, Halelu-Yah!

Halelu-Yah! Ku yabi Allahmmu, ya ku bayinsa,                                       Halelu-Yah!

    ku da ke jin tsoronsa, yaro da babba.                                            Halelu-Yah, Halelu-Yah!

Halelu-Yah! Gama Ubangiji Allahmmu Ma]aukaki shi ke mulki,             Halelu-Yah!

    mu yi murna da farinciki matu}a, mu kuma ]aukaka shi.             Halelu-Yah, Halelu-Yah!

Halelu-Yah! Don bikin [an Ragon nan ya zo,                                          Halelu-Yah!

    amaryatasa kuma ta kintsa.                                                           Halelu-Yah, Halelu-Yah!

Halelu-Yah! An yarje mata ta sa tufafi lallausa                                          Halelu-Yah!

    mai ]aukar ido, mai tsabta.                                                           Halelu-Yah, Halelu-Yah!

Halelu-Yah! [aukaka ga Uba da ga [a da ga Ruhu Mai Tsarki,               Halelu-Yah!

    yanzu da har abada.                                                                      Halelu-Yah, Halelu-Yah!

Afisawa 1:3-10

Yabo ya tabbata ga Allah da Uba * na Ubangijimmu Yesu Almasihu!

Gama ya yi mana albarka da kowace albarka mai ruhaniya * a mu}aman sama * ta kan Almasihu.

    Allah ya za~e mu ta kansa * tun ba a halicci duniya ba * mu zama tsarkaka, marasa aibu a gabansa.

        Ta }aunarsa ya }addara mu *ga zama 'ya'yansa

            ta kan Yesu Almasihu * bisa nufinsa na alheri,

                don mu yabi ]aukakar alherinsa * wanda ya ba mu kyauta hannu sake ta kan aunataccensa.

            Ta gare shi ne muka sami fansa * albarkacin jininsa, * watau yafewar laifuffukammu,

        bisa yalwar alherin Allah, * wanda ya yi mana falala.

    Da matu}ar hikima da basira, * ya sanasshe mu zuzzurfan al'amarin nufinsa

    bisa kyakkyawan nufinsa * da ya bayyana game da Almasihu.

Duk wannan shiri ne, don a cikar lokaci * a harha]a dukan abubuwa ta kan Almasihu,

watau, abubuwan da ke sama * da abubuwan da ke }asa.

Wahayin Yahaya 4:11; 5:9-10,12

Macancanci ne kai, ya Ubangiji Allahmmu, * ka sami ]aukaka da girma da iko.

Don kai ne ka halicci dukan abubuwa, * da nufinka ne suka kansance kuma aka halicce su...

    [an Ragon Allah, macancanci ne kai * ka ]auki littafin nan, * ka ~am~are hatimansa.

        Domin dā an kashe ka, * kuma ka fanso wa Allah mutane ta jininka * daga kowace kabila, da kowane harshe, da kowace jama'a, da kowace al'umma.

    Ka mai da su jama'a, * kuma firistocin Allahmmu, * suna kuwa mulki a duniya...

Macancanci ne [an Ragon nan da aka yanka * ya sami iko,

da wadata, da hikima, da }arfi, * da girma, da ]aukaka, da yabo.

Kolasiyawa 1:12-20

Ku gode wa Uba, * wanda ya maishe ku isa samun rabo

cikin gadon tsarkakan * da ke cikin haske.

    Ya tsamo mu daga mulkin duhu, * ya maishe mu ga mulkin }aunataccen Ðansa,

    wanda ta gare shi ne muka sami fansa, * watau gafarar zunubammu.

        Shi ne surar Allah mara ganuwa, * Magaji ne tun ba a halicci kome ba,

            Don ta gare shi ne aka halicci dukan kome, * abubuwan da ke sama da abubuwan da ke }asa, * masu ganuwa da marasa ganuwa,

                ko manyan mala'iku, ko masu mulki, * ko masarautu, ko masu iko,

            watau dukan abubuwa an halicce su ne ta kansa, * kuma shi ne makomatasu.

        Shi adimi ne gaba da kome, * kuma dukan abubuwa shi ke ri}e da su.

    Shi ne Kai ga jikin nan, watau ikiliziya, * shi ne Tushe,

    Na Farko cikin masu tashi daga matattu, * don ta kowane abu ya zama shi ne mafifici.

A gare shi dukan cikar Allah ta tabbata, * don Allah na farinciki da haka,

da nufin ta kansa * Allah ya sada dukan abubuwa da shi kansa,

na }asa ko na sama, * yana }ulla aminci ta jininsa na gicciye.

Wahayin Yahaya 11:17-18; 12:10b-12a

Mun gode maka, ya Ubangiji Allah, Ma]aukaki * wanda yake shi ne a yanzu, shi ne kuma a dā,

saboda ka ]auki ikonka mai girma, * kana mulki.

    Al'ummai sun husata, * hushinka kuwa ya sauko, * lokaci ya yi da za a yi wa matattu shari'a,

    a kuma yi wa bayinka, annabawa da tsarkaka sakamako, * da masu jin tsoron sunanka, * yaro da babba...

        Yanzu fa ceto, da }arfi, da mulki na Allahmmu, * da kuma ikon Almasihunsa sun bayyana.

        Don an jefa mai saran 'yan'uwammu }asa, * shi da ke saransu dare da rana a gun Allahmmu.

    Sun kuwa yi nasara da shi * albarkacin jinin [an Ragon nan, * da kuma albarkacin maganad da suka shaida,

    don ba su yi tattalin ransu ba, * har abin ya kai su ga kisa.

Saboda haka sai ku yi farinciki, ya ku sammai, * da ku mazauna ciki!

Wahayin Yahaya 15:3-4

Ayyukanka manya-manya ne, kuma masu ban mamaki, * ya Ubangiji Allah Ma]aukaki!

Hanyoyinka na gaskiya ne, kuma daidai suke, * ya Sarkin al'ummai.

    Wanene ba zai ji tsoronka ba, ya Ubangiji, * ya kuma ]aukaka sunanka? * domin kai ka]ai ne tsattsarka.

Dukan al'ummai za su zo * su yi maka sujada,

don hukuncinka na gaskiya * yā bayyana.

1 Bitrus 2:21-25

Almasihu ya sha wuya dominku, * ya bar muku misali * ku bi hanyarsa.

    Bai ta~a yin laifi ba faufau, * ba a kuwa ta~a jin yaudara a bakinsa ba.

    Da aka zage shi * bai rama ba,

    da ya sha wuya kuwa bai yi }wafa ba, * sai dai ya dogara ga wannan Mai shari'ar gaskiya.

    Shi da kansa ya ]auke zunubammu * a jika a kan gungume,

    don mu fita sha'anin zunubi ]ungum, * mu yi zaman aikin gaskiya.

    Da raunukansa ne * aka warkad da ku.

Dā kun sangarce kamar tumaki, * amma yanzu kun dawo ga Makiyayi, * kuma Mai kula da rayukanku.

Luka 1:47-55 Wa}ar Maryamu

Zuciyata na ]aukaka shi Ubangiji, * Allah Macecina * da shi ruhuna yake ta farinciki.

Domin fa shi ya dubi }asancinta ne baiwa tasa, * ai ga shi jama'a ta dukan zamani * mubarika ce za su ce mani nan gaba.

    Domin fa shi da ya ke yana Mai iko, * ai manya-manyan al'amurra yai mani, * sunansa ko labudda tsattsarka yake.

    Daga zamani har dai zuwa wani zamani, * tausansa na ga wa]anda ke tsoro nasa.

        Al'amari babba da }arfinsa ya yi, * ya watsa duk mutakabbirai sun watse.

    Ya firfitad da sarakuna a sarauta, * ya ]aukaka masu zaman }as}anci.

    Mayunwata ya yalwata da abubuwan alheri, * ya sallame su da babu, masu wadata.

Ya taimaka wa baransa Isra'ila, * domin yana tune dai da yin rahama tasa.

Ita ya yi alkawari ga kakannimmu, * tutur ga Ibrahim da duk zuriya tasa.

Luka 1:68-79 Wa}ar Zakariya

Ubangiji Allah na Isra'ila * a gare shi ne lalle yabo ke tabbata, * don ya kula, ya fanshi ma jama'a tasa.

Ya ta da Maceci mai iko domin mu, * daga zuriya ta baransa Dauda,

    yadda a tuntuni ya fa]a fa ta bakunan * su annabawa nasa tsarkakan nan:

    ya cece mu a gun su abokan gabammu, * har ma a hannun dukan ma}iyammu.

        Don nuna rahama ne ga kakannimmu, * ya tuna da alkawari nasa tsattsarkan nan.

        Shi ne rantsuwan nan wadda yai wa Ubammu Ibrahimu, * y cece mu gun su abokan gabammu,

        ya ba mu baiwa don mu dai bauta masa, * a gabansa ba a cikin halin tsoro ba ne,

        sai dai cikin tsarki da halin gaskiya, * dukan iyakar kwanakin nan namu.

    Kai kuma, yaro, za a kira ka annabi ne na Ma]aukaki, * za ka riga Ubangiji gaba, ka shisshirya hanyoyi nasa,

    ka sanad da su cetonsu su jama'a tasa, * watau na samun gafarar zunubai nasu.

Saboda tsananin rahamar Allahmmu, * daga can sama ne hasken alfijir zai keto mana,

har ya haskaka su na zaune can cikin duhu a bakin halaka, * har ma ya dai bishe mu hanyar lafiya.

Luka 2:29-32 Wa}ar Simiyan

Yanzu kam ya Mamallaki, * sai ka sallami bawanka lafiya, * bisa fa]an nan da ka fa]a.

    Don na ga cetonka zahiri, * da ka shirya a gaban kabilun nan duka,

Haske mai yi wa sauran al'ummai bu]i * abin kuma ]aukaka jama'arka Isra'ila.